in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Amurka ta yi barazanar janye tallafin da take baiwa kasashen da suka nuna adawa da batun birnin Kudus
2017-12-21 09:09:27 cri
Shugaba Donald Trump na kasar Amurka ya yi barazanar janye tallafin da kasarsa ke baiwa kasashen da suka goyi bayan kudurin MDD dake adawa da matsayin Amurka na ayyana birnin Kudus a matsayin babban birnin Isra'ila.

Kalaman Trump kan wannan batu na zuwa ne, bayan da jakadar Amurka a MDD Nikki Haley ta wallafa a shafinta na Twitter cewa, Amurka za ta tattara sunayen kasashen da suka soki matakin Amurka game da birnin Kududs a babban zauren MDD.

A ranar Litinin ne dai Amurkar ta hau kujerar naki kan kudurin MDD game da matsayin birnin Kudus, inda kasashe 14 mambobin kwamitin sulhu suka goyi bayan kudurin da kasar Masar ta gabatar, ban da Amurka.

A yau ne kuma babban zauren MDD zai yi wani taron gaggawa da ba safai yake yi ba domin tattauna matsayin birnin na Kudus, bayan da tun farko Amurka ta hau kujerer naki kan kudurin da kasar Masar ta gabatar,wanda ke bukatar Amurka ta janye batun ayyana birnin Kudus a matsayin hedkwatar kasar ta Isra'ila.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China