in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin na fatan bunkasa hadin gwiwa da kasar Gambia
2017-12-20 20:09:58 cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying, ta ce kasar ta Sin na fatan za a kai ga bunkasa amincewa da juna a fannin siyasa, tare da fadada hadin gwiwa a dukkanin fannoni da kasar Gambia, yayin ziyarar da shugaban kasar ta Gambia Adama Barrow zai kawo kasar.

Shugaban na Gambia dai zai gudanar da ziyarar ta sa ne daga ranar Laraba zuwa Talatar makon gobe, bisa gayyatar shugaban kasar Sin Xi Jinping.

Sin da Gambia sun sake maida huldar diflomasiyya ne a watan Maris na shekarar 2016, bayan dakatar da hakan tsawon shekaru 21.

Shugaba Barrow, shi ne shugaban Gambia na farko da zai ziyarci kasar Sin, tun bayan da sassan biyu suka maido da dangantakar diflomasiyya.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China