A talatar nan ne dai gidan talabijin na Al Akhbariya, ya rawaito rundunar sojin saman kasar ta Saudiyya na tabbatar da aukuwar wannan lamari. Sai dai rundunar ta ce makamin bai haifar da wata barna ko lahanta wani ba. Kana makamin bai kawo wata tangarda ga zirga zirgar jiragen saman kasar ta Saudiyya ba.
'Yan tawayen Houthi dai sun sha hakon biranen kasar ta Saudiyya, inda suke kai masu farmaki da makamai masu linzami tun daga shekarar 2015.