Cikin sanarwar, Mr Gutarres ya yi allah wadai da kakkausar murya kan harin da aka kai a wata majami'a dake birnin Quetta na lardin Balochistan, kana ya nuna juyayi ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu, da kuma fatan samun sauki ga wadanda suka jikkata.
Bugu da kari, ya ce, ya kamata a gurfanar da wadanda suka aikata wannan laifi a gaban kuliya.
A ranar 17 ga wata ne, aka kai hari kan wata majami'a dake birnin Quetta na lardin Balochistan a kudu maso yammacin kasar Pakistan, inda aka yi mumunan musayar wuta tsakanin jami'an tsaro da maharan, lamarin da ya haddasa rasuwar mutane a kalla 8, yayin da wasu fiye da 10 suka jikkata. (Maryam)