in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban JMEC ya bukaci IGAD da ta dawo da shirin wanzar da zaman lafiya a Sudan ta kudu
2017-12-18 09:00:23 cri

Shugaban hukumar hadin gwiwar sanya-ido da kimanta ci gaba (JMEC) ta kasar Sudan ta kudu Festus Mogae ya yi kira ga shugabannin kungiyar raya kasashen gabashin Afirka ko IGAD a takaice, da su hada kansu, tare da yin magana da murya guda, kana su karfafawa jagororin Sudan ta kudu gwiwar amfani da wannan dama wajen dawo da shirin zaman lafiyar kasar bisa turba.

Mr Mogae ya yi wannan kiran ne a jiya Lahadi, cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai yayin taron ministocin kungiyar IGAD karo na 59 da ya gudana a birnin Addis Ababan kasar Habasha.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China