in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
ECOWAS na taro a Najeriya game da matsayin kasar Morocco
2017-12-17 12:26:03 cri
A jiya Asabar aka bude taron koli na shugabannin kungiyar hadin kan tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika ECOWAS karo na 52 a Abuja, helkwatar Najeriya, domin tattauna batun kasar Morocco na neman zama mamba a kungiyar, da kuma duba batun yanayin tsaro a kasar Guinea Bissau.

Kasar Morocco ta mika bukatar zama mamba a ECOWAS, yayin da kasar Tunisiya take neman kasancewa mai sanya ido a cikin kungiyar.

A taron kolin ECOWAS karo na 51 wanda ya gudana a birnin Monrovia, na kasar Liberia a watan Yuni, aka amince za'a duba bukatar kasar Moroccon na neman zama mamba a kungiyar.

Yayin da hukumar gudanarwar kungiyar ta sahhalewa kasar Tunisiya ta zama mai sanya ido.

Hukumar gudanarwar kungiyar ta kuma tabbatar da cewa, ta bukaci kasar Mauritania data gabatar da bukatarta na neman komawa kungiyar ta ECOWAS.

Shugaban kasar Mauritanian Mohamed Ould Abdel Aziz, da shugaban kasar Tunisiya Beji Essebsi, zasu gabatar da jawabai a matsayin baki na musamman a lokacin bude taron kolin.

Taron kolin zai kuma tattauna game da yanayin siyasa da tsaro da ake ciki a kasar Guinea Bissau.(Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China