in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin tana goyon bayan warware batun Kudus bisa kudurin MDD
2017-12-14 20:23:05 cri
Yau Alhamis ne, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang ya bayyana a yayin taron manema labarai cewa, kasar Sin tana goyon baya a warware batun birnin Kudus bisa kudurin MDD da kuma matsayar da gamayyar kasa da kasa suka cimma kan batun. Kasar Sin tana fatan Isra'ila da Falesdinu za su hanzarta dawo wa kan teburin yin shawarwari, domin warware sabanin dake tsakaninsu yadda ya kamata.

Rahotanni na cewa, a jiya Laraba ne, mambobin kungiyar kasashen musulmi ta duniya (OIC) suka kira wani taro na musamman a birnin Istanbul na kasar Turkiya, inda suka zartas da wata sanarwa wadda ke yin kira ga gamayyar kasa da kasa da su amince da gabashin birnin Kudus a matsayin babban birnin Falesdinu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China