in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ana ci gaba da zaman dar dar a Afirka ta tsakiya
2017-12-14 11:34:57 cri
Wakilin musamman na babban magatakardar MDD a shiyyar Afirka ta tsakiya Francois Lounceny Fall, ya ce shiyyar na fuskantar yanayi na rashin tabbas a siyasance, baya ga kalubalen tattalin arziki, a yayin da a wasu lokutan, mahara masu dauke da makamai ke farwa fararen hula.

Mr. Lounceny Fall wanda ya bayyana hakan ga mambobin kwamitin tsaron MDD a jiya Laraba, ya ce warware wadannan matsaloli na bukatar hadin gwiwa daga masu ruwa da tsaki daga yankin, da ma na kasa da kasa.

Jami'in ya ce a kasashen Chadi, da Gabon, da jamhuriyar Congo, matsanancin yanayin tattalin arziki, tare da matsaloli na siyasa tsakanin tsagin gwamnatocin kasashen da na 'yan adawa, na ci gaba da kasancewa abun damuwa.

Ya ce ga misali a Kamaru, rabin yankunan kasar na fama da matsalar tsaro mai nasaba da ayyukan kungiyar nan ta Boko Haram, da masu nasaba da rigingimun dake aukuwa a jamhuriyar Afirka ta tsakiya, da kuma ta 'yan aware dake yankuna masu magana da yaren Ingilishi.

A daya hannun kuma, jamhuriyar Afirka ta tsakiya na fama da hare hare daga kungiyoyin masu dauke da makamai, inda sau da yawa, ake hallaka jami'an MDD dake aikin wanzar da zaman lafiya, da masu aikin jin kai a kasar.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China