in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gamayyar kasashen musulmi sun amince da gabashin Kudus a matsayin babban birnin Palastinu
2017-12-14 11:25:04 cri
A taron kolin kasashen musulmi wanda aka gudanar a ranar Laraba a Istanbul, sun bayyana gabashin Jerusalem a matsayin babban birnin kasar Palastinu, don yin raddi kan matakin da Amurka ta dauka na nuna fifiko kan Isra'ila.

Sanarwar da aka fitar a karshen taron kolin na wuni guda, wanda gamayyar kungiyar kasashen musulmi (OIC) ta shirya, ta bukaci dukkan kasashen musulmi na duniya su amince da tabbatar da kasar Palastinu kana su amince da gabashin Kudus a matsayin babban birnin Palastinawa.

Sanarwar ta ce, shugabanni da wakilan kasashen duniya da suka halarci taron sun yi Allah wadai da babbar murya da kuma bijirewa matakin da Amurkar ta dauka na kashin kanta, wanda shugaban kasar Donald Trump ya ayyana Jerusalem a matsayin babban birnin Israel.

Shugabannin sun bayyana matakin na Amurka a matsayin keta haddin al'ummar Palastinawa, da kuma yunkurin wargaza dukkan kokarin wanzar da zaman lafiya a yankin, da kuma kokarin haifar da bazuwar tsattsauran ra'ayin addini da ta'addanci, kana da yunkurin haddasa barazanar zaman lafiya da kwanciyar hankalin duniya baki daya.

Da yake jawabi a taron manema labarai a karshen taron kolin, shugaban Palastinawa Mahmoud Abbas yace, kasar Amurka ta nunawa duniya ba da gaske take yi ba game da yunkurin wanzar da zaman lafiya.(Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China