in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Israel ta kai hari kan Hamas don maida martani kan hare haren roka da aka kaddamar daga Gaza
2017-12-12 10:54:05 cri
Sojojin Israela sun sanar a jiya Litinin cewa, sun yi barin wuta kan magoya bayan kungiyar Hamas a matsayin mai da martani daga hare haren roka da ake kai mata daga zirin Gaza, daga yankunan da Palastinawa suka mamaye inda suke cigaba da yin barin wuta kan Isaralan, sai dai a cewarsu hare haren na Palastinawa bai cimma nasarar kaiwa inda suka son ya kai ba.

Mai magana da yawun sojin ya bayyana cikin wata sanarwa cewa, an gano wasu rokoki biyu da aka harba da yammacin ranar ta Litinin. Sai daga ba'a gano ko harin ya yi barna ba, kakakin sojin ya kara da cewa, dakarun sojin suna cigaba da bincike a yankin, domin gano burburshin rokokin da aka harba yankin.

Kasa da sa'a guda daga bisani, tankokin yakin Isaraila da jiragen saman yaki sun kutsa zuwa yankin zirin Gaza. Sun kaddamar da hare hare kan dakarun kungiyar Hamas dake kudancin zirin Gaza, inji kakakin sojin Isra'ilan.

Babu wata kungiya data yi ikirarin kaddamar da harin rokar wanda bai kai ga nasara ba, sai dai dakaraun sojin sunce sun dora alhakin duk wani tashin hankali da ya barke a zirin Gaza kan magoya bayan Hamas.

A kalla rokoki uku aka harba kan dakarun sojin a kudancin Israila a karshen mako, amma bai haddasa wata barna ba, amma sojojin Isra'ilan sun hallaka mutane 4 a zirin Gaza, inji kafafen yada labaran Palastinu.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China