A yau Talata ne aka kammala taron kasa da kasa na masu ruwa da tsaki game da yanar gizo ko Internet, karo na 4 a birnin Wuzhen dake gabashin kasar Sin.
Yayin taron na yini 3, an baje kolin sabbin fasahohi, da sassan ci gaba a fannin amfani da Internet. Wakilai daga gwamnatoci, da jagororin hukumomin kasa da kasa, da masana, da kwararru, da masu sana'o'i, sun halarci shirye-shirye 20, inda suka nuna nasarorin da suka cimma a fannin kirkire-kirkire, tare da tattauna sassan hadin gwiwa tsakanin su.
Manyan kamfanonin dake kerawa, da masu hada-hadar cinikayyar na'urorin fasahar sadarwa kamar su Apple, da Alibaba, da Huawei, sun halarci taron, tare da gabatar da sabbin fasahohin su.(Saminu Alhassan)