in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin kasar Sin ya bayyana matsayin kasarsa kan hana kungiyoyin 'yan ta'adda da rikice-rikice lalata kayan tarihi
2017-12-01 19:23:11 cri
A yayin taron yin rigakafi gami da hana kungiyoyin 'yan ta'adda da fadace-fadace lalata da kuma yin sumogar kayan tarihin da aka gada daga kaka da kakanninmu, wanda kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya ya yi jiya Alhamis, mukaddashin wakilin dindindin na kasar Sin dake MDD, Wu Haitao, ya gabatar da jawabi, inda ya bayyana matsayin gwamnatin kasar Sin kan wannan batu.

Wu ya ce, kayan tarihi da aka gada daga kaka da kakanni, suna bayyana nagartattun al'adu na bil'adama, kana, alamu ne na kasancwar al'adu iri daban-daban a duk fadin duniya. A 'yan shekarun nan, wasu kungiyoyin 'yan ta'adda da rikice-rikicen da suka barke sun kara lalata irin wadannan kayan tarihi a duniya, har ma wasu kungiyoyin 'yan ta'adda sun yi fasa-kwauri tare kuma da sayar da kayan tarihin don tattara kudade, aika-aikar da suka kawo barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a fadin duniya, kana, raina wa al'adun kasashe ne.

Wu ya kara da cewa, kamata ya yi kasa da kasa su yi aiki kafada da kafada, domin daukar kwararan matakan katse hanyoyin da kungiyoyin 'yan ta'adda suka bi wajen fasa-kwaurin kayan tarihi, da kiyaye kayan tarihi musamman a yankunan da suke fama da rikice-rikice.(Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China