in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta ci gaba da ba da taimako wajen warware batun Falesdinu ta hanyar siyasa
2017-12-01 13:34:56 cri
Jiya Alhamis ne, taron MDD karo na 72 ya tattauna batun Falesdinu da yanayin da ake ciki a yankin Gabas ta tsakiya.

A jawabinsa yayin taron, mukadashin zaunannen wakilin kasar Sin dake MDD Wu Haitao ya ce, batun Falesdinu batu ne mai muhimmanci a yankin Gabas ta tsakiya, shi ne kashin bayan tabbatar da zaman lafiyar yankin baki daya. A don haka, ya kamata a warware batun Falesdinu cikin yanayin adalci a dukkan fannoni, lamarin da zai dace da moriyar al'ummomin yankin, da kuma ba da gudummawa wajen kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya.

Ya kara da cewa, kasar Sin tana son yin hadin gwiwa da gamayyar kasa da kasa wajen neman hanyar warware matsalolin yankin Gabas ta tsakiya, domin shimfida zaman lafiya a yankin, da ma ci gaban yankin baki daya. (Maryan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China