in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasar Sin ya jinjinawa nasarorin da cibiyar raya masana'antu na kasar ta samu
2017-11-25 12:27:34 cri
Firaministan kasar Sin Li Keqiang ya gana da wakilan babban taro karo na 12 na cibiyar raya cinikayya da masana'atu ta kasar Sin da aka bude jiya Jumma'a, inda ya jinjinawa nasarorin da cibiyar ta samu.

Li Keqiang, ya ce cibiyar ta bada gagarumar gudunmawa wajen raya bangarori masu zaman kansu, wanda ya zama tubalin daidaita tattalin arzikin kasar da samar da hanyar samun kudin shiga tare da taka muhimmiyar rawa wajen inganta fasahohi da ciyar da harkokin kudi da tattalin arziki gaba.

Firaministan ya bukaci cibiyar a dukkan matakai ta samar da ci gaba na bai daya a bangarorin gwamnati da masu zaman kansu tare da inganta yanayin ciyar da bangarori masu zaman kansu gaba, domin tabbatar da samun karuwar hannayen jari a bangaren tare da raya sabon tsarin tattalin arziki.

Ya kara da cewa, ya kamata cibiyar ta kiyaye sabbin manufofin tattalin arziki yayin da take kokarin tabbatar da inganci da adalci da dorewarta tare da samar da ingantattun hidimomi a fannin kasuwanci.

Cibiyar raya masana'antu da cinikayya ta kasar Sin, da ta kunshi masana'antu da mutane daga bangarorin cinikayya da masana'antu masu zaman kansu, cibiya ce mai zaman kanta da aka kafa a shekarar 1953. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China