in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An samu fitowar jama'a da yawa a zaben majalisun yankunan kasar Algeriya
2017-11-24 10:12:20 cri
Da misalin karfe 9 na yamma agogon kasar Aljeriya ne aka kammala zabukan majalisun yankunan kasar, bayan da hukumomi a kasar Algeriyar suka amince da karin sa'a guda domin baiwa al'ummar kasar karin lokacin kada kuri'unsu.

Ministan cikin gidan kasar Noureddine Bedaoui ya sanar da cewa an samu fitowar masu kada kuri'u da kashi 33.26 bisa 100 a zabukan shugabannin kananan hukumomin, yayin da aka samu fitar masu kada kuri'a da kashi 34.46 bisa 100 na zabukan majalisar kansilolin yankunan kasar, yayin da ya rage sa'oi biyu a kammala zabukan.

A shekarar 2012, an samu fitowar masu kada kuri'un a zabukan shugabannin kananan hukumomin kasar da kashi 28 bisa 100, yayin da aka samu fitar masu kada kuri'a da kashi 27 bisa 100 na zabukan majalisar kansilolin yankunan kasar.

A nasa bangaren, shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasar, Abdelouahab Darbal, ya ce an samu kura-kurai sama da 600 a zabukan, sai dai ya ce basu shafi sahihancin yadda aka gudanar da zabukan ba.

Kimanin 'yan kasar Algeriyan miliyan 23 ne suka cancanci kada kuri'a a zaben tsakanin 'yan takara 165,000 wadanda zasu wakilci kananan hukumomi da majalisun dokokin yankunan kasar 1541. Sama da 'yan takara 16,000 ne suka fafata a zabukan kujerun majalisun dokokin kananan hukumomin kasar 48.

Kimanin jami'an 'yan sanda 180,000 aka tura yankunan kasar don sanya ido a zaben.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China