in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kurdawan Iraqi sun amince da martaba umarnin kotu
2017-11-15 11:18:45 cri
Gwamnatin 'yankin Kurdawan Iraqi, ta ce za ta amince da martaba umarnin kotun tarayyar kasar, wadda ta jaddada cewa babu wata dama da wani yankin kasar ke da ita ta ballewa daga tarayyar kasar.

Wata sanarwa da mahukuntan yankin na Kurdistan suka fitar, ta ce gwamnatin yankin ta amince da fassarar da kotun tarayyar kasar ta yi wa sashe na 1 na kundin tsarin mulkin kasar, game da dakile ballewar yankunan kasar, to sai dai kuma ta ce hakan zai zamo dan ba ne ga burin yankin, na hawa teburin shawarwari, domin warware dukkanin takaddama mai nasaba da salon jagorancin kasar ta Iraqi.

A ranar 6 ga watan Nuwambar nan ne, kotun kolin kasar ta yanke hukunci game da batun neman 'yancin kan yankin na Kurdistan, tana mai tabbatar da cewa, ba wani sashe na kundin da ya amince da ballewar wani yankin kasar ba.

Hakan kuwa ya biyo bayan bukatar fashin baki game da tanaje tanajen kundin tsarin mulkin kasar ne, wanda gwamnatin tarayyar Irakin ta gabatarwa kotun. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China