in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kamfanin CGGC ya kulla kwangilar samar da wutan lantarki da Najeriya
2017-11-14 19:23:51 cri
Katafaren kamfanin gine-gine na kasar Sin, kamfanin da ya gudanar da aikin gina babbar madatsar ruwa ta kasar Sin(CGGC) ya bayyana a yau Talata ce, ya sanya hannu kan kwangilar samar da wutan lantarki bisa karfin ruwa da gwamnatin Najeriya wadda darajarta ta kai dala biliyan 5 da miliyan 792.

Kamfanin mai hedkwata a birnin Wuhan na kasar Sin, ya bayyana a cikin wani sako da ya wallafa a adireshinsa na Wechat cewa, aikin samar da wutar lantarki na Mambila, shi ne aiki mafi girma da kamfanin yake gudanarwa a tarayyar Najeriya kana aikin samar da wutar lantarki bisa karfin ruwa mafi girma da kamfanonin kasar Sin suka taba gudanarwa a ketare.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China