in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wani masani a Afrika ya yi gargadin yin taka tsan-tsan game da shirin cikini maras shinge
2017-11-14 10:52:25 cri
Wani masanin harkokin cinikayya ya gargadi kasashen nahiyar Afrika dasu yi hattara wajen aiwatar da shirin nan na kafa yankin ciniki maras shinge wanda aka gabatar dashi, don gudun kada ya haifar da illa a maimakon amfanarwa.

Dr Francis Mangeni, masanin harkokin ciniki kuma daraktan kasuwanci na kasuwannin gabashi da kudancin Afrika yace, kamata ya yi kasashen su yi taka tsan-tsan game da kafa yankin ciniki maras shinge na nahiyar wato (CFTA) a takaice.

Ya bayyana cewa, yarjejeniyar kafa tsarin na CFTA zai cika ne a watan Disamba.

A wata sanarwa da masanin ya fitar yace, akwai matukar hadari dake tattare da aiwatar da shirin cikin gaggawa, yace an tsara shirin na CFTA ne ta yadda ba'a yi la'akari da wasu batutuwa ba musamman wadanda suka shafi batun tsawwala kudaden haraji a manyan hajojin wanda hakan zai iya zama koma baya ga harkokin cinikayya a tsakanin kasashen nahiyar ta Afrika. (Ahmad)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China