in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Baje kolin kasar Sin da Afrika zai samar da wani sabon dandalin inganta hadin gwiwa a bangaren masana'antu
2017-11-14 10:05:07 cri
Hukumar inganta cinikayya da kasashen ketare ta kasar Sin CCPIT, ta ce taron baje kolin Sin da Afrika dake karatowa, zai karfafa cinikayya tsakanin bangarorin biyu tare da inganta kwarewar bangaren masana'antu.

Mataimakin shugaban hukumar CCPIT Chen Zhou, ya ce baje kolin na hadin gwiwa tsakanin kasar Sin da Afrika domin inganta ayyukan masana'antu da hukumar CCPIT ta shirya, zai gudana ne a Nairobin kasar Kenya daga ranar 13 zuwa 16 ga watan Decemba.

Chen Zhou ya ce an kammala dukkan shirye-shiryen gudanar da baje kolin da CCPIT ta shirya a nahiyar Afrika a karon farko.

Ya ce jimilar kamfanonin kasar Sin 56 ne za su shiga baje kolin inda za su nuna kayayyaki masu matukar inganci da fasahar zamani wajen sarrafa amfanin gona da manyan Injina da na shimfida layin dogo da ginin titi, da samar da hanyoyin sadarwa.

Ya kara da cewa, yayin da Afrika ke da arzikin albarkatu da jama'a, kuma take kan matakin fara raya bangaren masana'antu, kasar Sin na da fasaha da injina da kwarewa da kuma kudin da za ta taimakawa nahiyar cimma burinta na samun ci gaba mai dorewa ta hanyar dogaro da kanta. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China