in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Aljeriya ya samu galaba a yakin da take yi da ta'addanci a kasar
2017-11-07 11:30:29 cri
Mahukuntan Aljeriya sun bayyana cewa, sun samu galaba a yakin da suke yi da ta'addanci a kasar, kuma yanzu haka kasar ta daura damarar yaki da masu tsattsauran ra'ayin addini.

Ministan harkokin addini na kasar Mohamed Aissa shi ne ya bayyana hakan, yana mai cewa, masallatai da Limaman kasar sun dauki matakan da suka dace na toshe duk wasu kafofin yada tsattsauran ra'ayin addini a kasar, inda yanzu suke nunawa jama'a tsari da ka'idjojin addinin musulunci na zahiri.

Ministan ya ce, malaman addini suna taka muhimmiyar rawa wajen yada koyarwar addinin musulunci yadda ya kamata, sabanin hanyoyi marasa kyau da kasar ta tsinkin kanta a baya.

Aljeriya dai ta fuskanci ayyukan ta'addanci a shekarun 1990, tun lokacin da kasar ta bullo da matakan yaki da ayyukan ta'addanci a fadin kasar. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China