in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Morocco zata harba tauraron dan adam mai bincike a karon farko
2017-11-05 13:13:40 cri
Kafafen yada labaran kasar Morocco sun rawaito cewa, kasar ta shirya tsab don harba tauraron dan adam mai bincike a karon farko.

Gidan talabijin na Morocco Medi1TV ya rawaito cewa, an yiwa tauraron dan adam din lakabin "Mohammed VI-A," wanda ake saran harbawa sararin samaniya.

Za'a harba tauraron dan adam din ne a cibiyar harba tauraron dan adam ta Guiana, kuma Thales Alenia Space da Airbus sun samar da tauraron ne cikin hadin gwiwa.

A cewar kamfanin Arianespace group, tauraron dan adam din na Mohammed VI-A, za'a yi amfani dashi ne wajen gudanar da aiyukan binciken taswira da filaye, da safiyo, da bincike a fannin aikin gona, da rikakafin afkuwar bala'u, da kare muhalli, da kiyaye kwararowar Hamada, da kuma aikin tsaron kan iyakokin kasar da tekunan kasar.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China