in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar UNHCR ta bukaci kwamitin sulhu na MDD ya kawo karshen abubuwan dake haddasa gudun hijira
2017-11-03 10:50:33 cri
Babban Jami'in hukumar kula da 'yan gudun hijira na MDD Flippo Grandi, ya bukaci kwamitin sulhu na Majalisar ya kawo karshen abubuwan dake haifar da rikicin dake daidaita jama'a a fadin duniya.

Da yake jawabi ga kwamitin, Flippo Grandi ya gabatar da ainihin abun da duniya ke fuskanta a yanzu, inda ake samun sabbin rikice-rikice dake haifar da gudun hijira a kusan dukkan sassan duniya.

Ya bukaci kwamitin ya mara baya ga matakan kawo karshen abubuwan dake haddasa rikici.

Har ila yau, ya yi tsokaci kan batun yaki da safarar bil adama tare da ci gaba da kare 'yan gudun hijira yayin da ake kokarin shawo kan rikice-rikice.

Flippo Grandi ya ce adadin mutanen da suka tserewa matsugunansu bisa tilas a fadin duniya na tunkarar miliyan 66, adadin da ya karu daga miliyan 42 a shekarar 2009. Ya ce adadin ya kunshi 'yan gudun hijira miliyan 17.2 dake karkashin kulawar hukumarsa, inda aka samu karuwar adadin da kaso 70 cikin shekaru 8. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China