in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta horas da likitocin zuciya sama da 60 a kasashen ziri daya da hanya daya
2017-10-31 10:21:37 cri
Wani jami'in kungiyar masana cutukan zuciya na kasar Sin ya bayyana cewa, kasar ta bada horo ga likitocin da suka kware a fannin cutukan zuciya sama da 60 daga kasashe 6 dake kan hanyar ziri daya da hanya daya tun daga watan Mayu.

Liu Lu, shugaban kungiyar masana cutukan zuciya na kasar Sin ya bayyana cewa, likitocin daga kasashen Indonesia da Mauritius sun samu horo a wasu asibitoci daga biranen Beijing da Shanghai.

A shekarar data gabata ne hukumomin lafiya na kasar Sin suka amince da shirin bada horon domin inganta fasahar likitocin kasashen dake kan hanyar ziri daya hanya daya.

Kwasa-kwasan sun fara ne daga mako guda zuwa watanni 3. Sai kuma wanda ya yafa daga watanni 6 zuwa shekara guda.

Ana sa ran wasu karin kasashen dake kan hanyar ziri daya da hanya daya za su amfana da shirin.

Bayan cigaban da ta samu shekaru 30 a fannin bada tallafi game da cutukan zuciya, kasar Sin ta samu babban matsayi na yin gogayya a matakin kasa da kasa a fannin kimiyyar cutukan zuciya.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China