in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane 10 ne suka hallaka sakamakon fashewar abubuwa a Somalia
2017-10-26 10:36:27 cri
A kalla mutane 10 ne suka mutu sannan wasu 16 kuma suka jikkata, a sakamakon fashewar wasu abubuwa da aka binne a karkashin kasa, inda lamarin ya shafi tawagar dakarun wanzar da zaman lafiya na kungiyar tarayyar Afrika dake aiki a Somali (AMISOM), a kudancin Mogadishu babban birnin kasar Somali.

Wani jami'in tsaro ya shedawa kamfanin dillancin labaran kasar Sin Xinhua ta wayar tarho cewa, lamarin ya faru ne a wani yanki tsakanin Arbiska da Lafole a kusa da garin Afgoye, dake da tazarar kilomita 30 daga Mogadishu babban birnin kasar.

Mai Magana da yawun dakarun na AMISOM Wilson Rono, ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce an kashe mutanen ne a lokacin fafatawa tsakanin dakarun AU da mayakan Al-Shabaab.

Rono yace AMISOM ta yi hasarar sojinta guda kuma wani sojin guda ya samu raunuka.

Amma wata majiya mai zaman kanta ta ambato cewa, a kalla sojojin AU 3, da wasu malamai 2, da dalibai, da masu gadi da kuma mayakan Al-Shabaab 4 ne aka kashe a lokacin arangamar.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China