in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Guterres ya yi maraba da daddale yarjejeniyar sulhu da kungiyoyin Fatah da Hamas suka yi
2017-10-13 10:24:32 cri

Babban sakataren MDD Antonio Guterres, ya gana da shugaban Palestinawa Mahmoud Abbas ta wayar tarho, inda ya taya shi murnar daddale yarjejeniyar sulhu da kungiyoyin Fatah da Hamas suka yi.

Wata sanarwa da ofishin kakakin babban sakataren ya fitar, ta ce Antonio Gutarres ya yi farin ciki matuka bisa ci gaban da gwamnatin Palestinu ta samu a zirin Gaza, ya na mai jinjinawa gwamnatin kasar Masar bisa kokarin shiga tsakanin da ta yi kan batun.

Antonio Guterres ya ce, a shirye MDD take ta taimakawa gwamnatin Palestinu yayin da take gudanar da harkokin zirin Gaza, inda ya jaddada muhimmancin warware rikicin jin kai a zirin, musamman ma wajen samar da wutar lantarki, da jigilar kayayyakin jin kai.

Kungiyoyin Fatah da Hamas sun tattauna a birnin Alkahira na kasar Masar tsawon yini biyu, inda a jiya suka cimma yarjejeniyar sulhu.

Kungiyar Fatah ce za ta fara gudanar da harkokin zirin Gaza a maimakon Hamas tun daga ranar 1 ga watan Disamban dake tafe.(Jamila)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China