in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Palesdinu: Sabon shirin habaka matsugunan Yahudawa na nufin yin yaki ga "shirin kafa kasashe biyu"
2017-10-12 10:28:19 cri
A jiya Laraba, Mr. Riyad Malki, ministan harkokin wajen kasar Palesdinu ya bayyana cewa, sabon shirin da gwamnatin Isra'ila ta fitar na gina karin dubban gidaje ga Yahudawa a yankin dake yammacin gabar kogin Jordan, ya kasance tamkar wata sanarwar tada yaki ne ga "shirin kafa kasashe biyu".

Mr. Malki ya ce, ba za'a amince ko kuma yarda da matakin Benjamin Netanyahu ba, firaministan gwamantin Isra'Ila ya saci moriyar al'ummar Palesdinu ya kara saurin gina matsugunan Yahudawa domin cimma burinsa na samun nasara a yakin takara tsakanin jam'iyyun siyasar Isra'ila ba.

Mr. Malki ya kara da cewa, yanzu bangaren Palesdinu na jira bangaren Amurka ta dakatar da shirin Netanyahu. Idan ba zai yi hakan ba, bangaren Palesdinu zai dauki matakai nasa ga ayyukan gina matsugunan Yahudawa da ake hanzarta ginawa.

Yanzu gwamnatin Isra'ila tana son amincewa da shirin gina karin gidaje 3829 ga Yahudawa a wasu yankunan dake yammacin kogin Jordan. An yi hasashen cewa, za a amince da shirin a yayin taron babban kwamitin tsara shirye-shirye na hukumar kula da harkokin al'umma ta Isra'ila da za a shirya a ran 16 ga watan nan. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China