Rundunar 'yan sandan birnin ta ce an kama mutum 1 bayan aukuwar hatsarin.
Sanarwar da rundunar ta fitar ta ce al'amarin batu ne da ya shafi ka'idojin titi, kuma ba shi da alaka da ta'addanci, ta na mai cewa ana ci gaba da bincike.
Ta ce mutane 11 ne aka samu a wajen da raunaka daban-daban, kuma tuni an kai 9 daga cikinsu asibiti, ciki har da mutumin da aka tsare.
Sanarwar ta kuma kara da cewa, raunakan da mutanen suka samu ba masu ta da hankali ba ne. (Fa'iza Mustapha)