in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan ta bayyana takaicin kasancewa cikin jerin kasashen da Amurka ta ayyana a matsayin masu safarar bil adama
2017-10-06 12:29:11 cri
Gwamnatin Sudan ta bayyana takaici game da sanya ta da Gwamnatin Amurka ta yi, cikin jerin kasashen da ake zargi da gazawa wajen yaki da safarar bil Adama.

Wata sanarwa da ma'aikatar harkokin wajen kasar ta fitar jiya, ta jadadda kudurin gwamnatin kasar na yaki da matsalar safarar bil Adama bisa dokokin kasar, musamman dokar yaki da safarar bil adama ta 2014, baya ga kudurinta na amfani da dokokin kasa da kasa dake da alaka da mastalar.

Ma'aikatar ta bayyana wasu matakan da Khartoum ta dauka na yaki da safarar bil adama, ta na mai cewa, gwamnatin ta kafa cibiyoyin karba da kula da mutanen da aka yi safararsu tare da samar musu da tallafi.

Har ila yau, ta jadadda kudurin kasar na ci gaba da hada hannu da al'ummomin kasashen waje wajen yaki da matsalar.

A ranar 30 ga watan Satumban da ya gabata ne fadar white House ta Amurka, ta ayyana tare da kara wasu kasashe 6 da suka hada da Sudan da Iran da Venezuela da Jamhuriyar Demokradiyyar Congo da Equatorial Guinea da kuma Sudan ta kudu cikin jerin kasashen da suka gaza yaki da safarar bil Adama. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China