in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban yankin Kurdawa ya sake nanata kudurinsu na gudanar da kuri'ar raba gardama
2017-09-25 10:50:11 cri
A jiya Lahadi ne shugaban yankin Kurdawa Masoud Barzani ya sake nanata kudurinsu na gudanar da kuri'ar raba gardama kamar yadda ake shirya a yau Litinin, game da nemawa yankin na Kurdawa kwarya kwaryar 'yancin cin gashin kai.

Barzani ya shaidawa taron manema labarai cewa, babu gudu babu ja da baya game da shirinsu na kada kuri'ar jin ra'ayin jama'a kan wannan batu, duk da kiraye-kiraye da matsin lambar da suke fuskanta daga gwamnatin Bagadaza, da kasashe makwabata da Amurka kan su dakatar da kada kuri'ar ta yadda za a koma kan teburin sulhu.

Barzani ya ce, tattaunawar da suke yi da gwamnatin Bagadazan ta rushe, har ma firaministan Iraki Haider al-Abadi ya mayar da martani cikin fushi, inda ya nanata cewa, ba ya goyon bayan shirin kuri'ar jin ra'ayin jama'a game da kwarya kwaryar nemen 'yancin kai na yankin.

A don haka, Barzani ya ce yanzu kan bakin alkalami ya riga ya bushe. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China