in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
A Najeriya 'yan tada kayar baya sun kaddamar da hari kan wani kwale-kwale
2017-09-24 13:52:33 cri
Wasu da ake zargin mayakan tsagerun yankin Niger Delta ne sun kaddamar da hari kan wani kwale-kwale inda suka hallaka mutane 3.

Asinim Butswat, kakakin rundunar 'yan sandan jahar Bayelsa ya tabbatar da afkuwar lamarin, yace wani dan sanda guda ya bace a lokacin kaddamar da harin.

A cewarsa, tuni aka tura jami'an gudanar da bincike don gano dan sanda da ya bace, kana dukkan jami'an tsaro a karamar hukumar Ijaw na zaune cikin shirinn ko-ta-kwana sakamakon faruwar lamarin.

Kwale-kwalen wanda ke dauke da tawagar jami'an tsaro da fararen hula wadanda ke yin rakiya ga babban jirgin ruwan dake dakon danyen mai, an kaddamar da harin kansa ne a ranar Juma'ar data gabata, harin da ake zargin masu fashin jirgin ruwa da kaddamarwa a kan tekun Ekebiri dake kudancin karamar hukumar Ijaw a jahar Bayelsa.

Mai Magana da yawun 'yan sandan ya shedawa 'yan jaridu cewa tuni aka tura jami'an kai dauki zuwa wajen da lamarin ya faru, kuma sun yi nasarar ceto 8 daga cikin mutanen da aka illata a cikin kwale kwalen.

Wannan harin ya zo ne makonni 3 bayan wani musayar wuta da aka yi a wani gidan sojoji dake kan tekun, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 2 a kudancin karamar hukumar ta Ijaw.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China