Gwamnatin kasar Mexico ta ce, adadin mutanen da suka rasa rayukansu a sanadiyyar girgizar kasa mai karfin maki 7.1 da ta auku a ranar Talata, ya karu zuwa 273.
Rabin mace-macen ya auku ne a birnin Mexico City, inda kusan gine-gine 40 suka rushe, yayin da sauran suka auku a kewaye da jihohi dake kusa da birnin.
Akwai yiwuwar adadin zai karu yayin da ake ci gaba da aikin ceto, inda ake zakulo gawarwaki daga cikin baraguzan gine-gine da suka rushe a sanadiyyar girgizar kasar. (Fa'iza Mustapha)