in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Sudan ya bukaci mazauna yankin Darfur su mika makamansu
2017-09-22 10:03:50 cri

Shugaban Sudan Omar Al-Bashir, ya bukaci mazauna yankin Darfur da su mika makamansu ga gwamnati bisa radin kansu, kafin gwamnati ta fara karba da karfi.

Da yake jawabi ga wani taron jama'a a birnin Nyala, babban birni jihar Darfur ta Kudu, shugaba Al-Bashir ya ce, da gaske suke game da batun kwace makamai, kuma abu mafi dacewa ga duk wani da ya mallaki bindiga shi ne ya mika bindigar ga hukuma.

Ya kara da cewa, dole ne duk wani da ya boye makami ya mika shi ga gwamnati bisa radin kansa. (Fa'iza Msutapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China