in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Sudan ya yi gargadi game da safarar makamai a kan iyakar kasar da Chadi
2017-09-20 10:09:05 cri

Shugaban kasar Sudan Omar al-Bashir ya yi gargadi game da safarar makamai da 'yan tawaye masu dauke da makamai a kan iyakar kasar ta Sudan da jamhuriyar Chadi.

Al- Bashir ya bayyana cewa, kan iyakar kasashen biyu ba waje ne na yin safarar makamai ba, sai dai waje ne na yin musaya domin amfanin kasashen. Ya bayyana hakan ne a lokacin wani rangadi wanda ya fara a yankin Darfur a ranar Talata, yankin dake fama da yakin basasa tun daga shekarar 2003.

Ya bayyana hadin gwiwar dakarun kasar Sudan da na Chadi a matsayin wani abin koyi na hadin gwiwa tsakanin kasashen dake makwabtaka da juna, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi ga dandazon jama'a a El Geneina, babban birnin jihar yammacin Darfur.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China