in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin da MDD sun alkawarta bunkasa hadin gwiwa
2017-09-19 13:46:21 cri
Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, da babban magatakardar MDD Antonio Guterres, sun sha alwashin bunkasa dangantaka dake tsakanin Sin da MDD, tare da daukar matakan shawo kan wasu batutuwa da suka shafi sassan biyu. Jami'an sun bayyana wannan buri ne yayin wata ganawa da suka yi a jiya.

Da yake tsokaci game da hakan, Mr. Wang ya yi fatan ganin MDD ta kara fadada rawar da take takawa a harkokin duniya, musamman a wannan lokaci da kalubale ke daduwa a sassa daban daban. Ya ce Sin za ta hada kai da MDD wajen ganin an inganta dangantakar kasa da kasa, da zuba karin jari domin samar da ci gaba, tare da daukar matakan wanzar da zaman lafiya, duka dai da nufin dakile matsaloli da duniya ke fuskanta.

Har wa yau, a yayin ganawar sa da Miroslav Lajcak shugaban zama na 72 na MDDr dake gudana a yanzu haka, ministan na harkokin wajen kasar Sin, ya jinjinawa kokarin majalissar bisa managartan manufofi da take aiwatarwa.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China