Karkashin wani shirin hadin gwiwa na gwamnati da hukumomi masu zaman kansu da UNICEF da hukumar samar da ruwa ta yankin Puntland, da sashen samar da makamashi da albarkatun kasa, da kamfanin GUMCO, za su gudanar da aikin gyaran tankokin ruwan sha da kuma shimfida bututun ruwa sama da mita dubu 10, domin gyaran hanyoyin samar da ruwan sha da suka lalace a garin Bosasso. (Ahmad Fagam)