A jiya Lahadi ne kungiyar Hamas ta Palasdinu, ta sanar da cewa, za ta wargaza kwamitin kula da harkokin zirin Gaza, kuma ta amince da shirya babban zabe a Palesdinu, kuma tuni kungiyar Fatah da sauran jam'iyyun siyasa na Palestinu suka yi maraba da wannan kuduri na Hamas.
A cikin sanarwar, Hamas ta amince da gwamnatin sulhun da Palesdinu ta kafa game da harkokin zirin Gaza, tare kuma da aiwatar da yarjejeniyar sulhun da ta daddale da Fatah a birnin Alkahira na kasar Masar a shekarar 2011. (Jamila)