An sace jami'an 3 ne a ranar 4 ga watan nan a jihar Zamfara dake arewa maso yammacin kasar, a lokacin da wasu 'yan bindiga da ba a san ko su waye ba suka yi wa wani karamin ofishin 'yan sanda tsinke a kauyen Tsafe na jihar.
Kwamishinan 'yan sandan jihar Shaba Alkali, ya ce daya daga cikin jami'an ya samu rauni sakamakon harbin da mutanen suka yi.
A cewarsa, rundunar da hadin gwiwar sauran hukumomin tsaro na aiki domin tabbatar da kama 'yan bindigar. (Fa'iza Mustapha)