Shugabar majalisar dokokin Gambia za ta kawo ziyarar aiki kasar Sin
2017-09-16 13:27:42
cri
Shugabar majalisar dokokin kasar Gambia Mariam Jack Denton za ta kawo ziyarar aiki kasar Sin daga ranar 18 zuwa 23 ga watan nan da muke ciki, bisa gayyatar da shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin Zhang Dejiang ya yi mata. (Maryam)