Kakakin rundunar sojin saman kasar Tokunbo Adesanya, ya bayyana a jiya cewa, sun yi ammana mayakan kungiyar da ba a san adadinsu ba sun mutu yayin harin da aka kai ranar Alhamis da ta gabata.
A cewarsa, wuta ta tashi a ginin da aka kai wa harin a yankin arewacin jihar Borno dake iyaka da tafkin Chadi, inda ya ce wuri ne da aka san cewa akwai mayakan Boko Haram da dama.
Tokunbo Adesanya ya kara da cewa, jirage biyu ne suka kai harin, a ci gaba da luguden wuta kan gidajen da ake zargin muhalli ne ga mayakan Boko Haram da Rundunar sojin saman ta ke yi.(Fa'iza Mustapha)