in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan da Masar sun ratabba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna ta sanya ido kan girgizar kasa da hakar ma'adinai
2017-09-11 10:41:29 cri

Ma'aikatar kula da albarkatu ta Sudan da hukumar binciken kimiyya da albarkatun kasa ta Masar sun ratabba hannu kan wata yarjejeniyar fahimtar juna don yin hadin gwiwa ta fuskar sanya ido kan girgizar kasa da hakar ma'adinai da mai.

Cikin wata sanarwa da ya fitar, darakta janar na hukumar binciken ta Masar Mohammed Abu Fatma, ya ce yarjejeniyar da aka ratabbawa hannu a jiya Lahadi, za ta tanadi musayar bayanai tsakanin Sudan da Masar a matakin yanki, da ma duniya baki daya.

Da yake bayyana yarjejeniyar a matsayin mai muhimmanci, ya kuma yi bayanin cewa, ta samar da wata taswirar fasahar karkashin kasa, wadda ke da matukar muhimmanci da za ta iya bibiyar gudanar ruwan kogin Nile, musammam a lokacin ambaliya.

Yarjejeniyar ta kuma tanadi ba da horo ga jami'ai da bibiyar madatsu da ma'adanan ruwa da hakar ma'adinai da kuma ginin hanyoyi. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China