in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An zartas da kudurin sanya takunkumi ga wadanda ke dagula yanayin zaman lafiya a Mali
2017-09-06 15:14:47 cri

A jiya Talata ne kwamitin sulhun MDD ya zartas da wani kuduri mai lambar 2374, inda aka tsai da kudurin cewa, za a sanya takunkumi ga mutane ko kamfanoni dake daukar matakan gurgunta yunkurin shimfida zaman lafiya a kasar Mali.

Takunkumin dai zai iya zama na hana tafiye-tafiye, da kuma hana amfani da kadarorinsu, kana domin aiwatar da takunkumin, za a kafa wata hukuma ta musamman.

A dai wannan, babban sakataren MDD Antonio Guterres ya fitar da wata sanarwa, inda ya yi suka ga harin da aka kaiwa ayarin motocin rundunar sojojin kiyaye zaman lafiya dake Mali a jiya Talata, harin da ya haddasa rasuwar sojojin kiyaye zaman lafiya guda biyu, tare kuma da jakkata wasu saura guda biyu.(Jamila)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China