in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Trump na shawarta yanke alaka da kasashe masu ma'amala da Koriya ta Arewa
2017-09-04 10:23:09 cri
Shugaba Donald Trump na Amurka, na duba yiwuwar yanke dukkanin alakar cinikayya da kasashen da ke ma'amala da Koriya ta Arewa. Mr. Trump ya bayyana hakan ne a jiya, bayan da kafofin watsa labarun Koriyar ta Arewan suka yi ikirarin cewa, kasar ta gwada wani makami mai kunshe da iskar gas mai guba ta Hydrogen, wanda za a iya harbawa daga wata nahiya zuwa wata.

Cikin wani sako na Tweeter, Mr. Trump ya ce kalamai da ayyukan mahukuntan Koriya ta Arewa na da matukar hadari, don haka ya ce zai gana da shugaban ma'aikata na fadar White House John Kelly, da sakataren tsaro James Mattis, tare da wasu kusoshin rundunar sojin kasarsa domin tattauna halin da ake ciki.

A wani ci gaban kuma, wata sanarwa daga ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin, ta bayyana rashin amincewar kasar da matakin na Koriya ta Arewa, tana mai Allah wadai da gwajin wannan makami na nukiliya.

Sanarwar ta ce Koriya ta Arewa ta yi kunnen uwar shegu da kiraye kirayen da kasashen duniya ke mata, na kauracewa gwajin makaman nukiliya, don haka ko alama, gwamnatin Sin ba ta goyi kasar game da wannan batu. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China