in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Taron shugabannin kungiyar BRICS a birnin Xiamen zai habaka hadin gwiwar dake tsakanin kasashen da sauran kasashen duniya
2017-09-02 13:29:01 cri
Za a yi taron shugabannin kasashen BRICS karo na 9 a birnin Xiamen na kasar Sin a gobe Lahadi 3 ga wata, inda shugabannin kasashen biyar masu samun saurin ci gaban tattalin arziki a duniya za su halarci taron cikin hadin gwiwa.

Kuma ana sa ran ba da sabuwar shawara dangane da hadin gwiwar kasashe masu tasowa a wajen taron.

Ana ganin cewa, taron shugabanni ta wannan karon, zai habaka hadin gwiwar kasashen BRICS, inda kuma ake son ci gaba da tattaunawa kan shawarar "BRICS+" da kasar Sin ta fitar.

Ana iya samun bayani kan taron shugabannin kasashen BRICS karo na 9 a shafin intanet na musammam da aka samar don taron, inda kasar Sin ta ba da shawarar kyautata tsarin hadin gwiwar kasashen, ta fuskar habaka hadin gwiwar dake tsakaninsu, har ma da sauran kasashe abokan hulda, ta yadda za a samar da wani tsari da kasar Sin ta kira da "BRICS+".

Bugu da kari, a halin yanzu, yin shawarwari da hadin gwiwa da kasashe masu tasowa domin neman ci gaba tare ya kasance wata kyakyyawar al'ada ta taron shugabannin kasashen BRICS. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China