Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da takwaransa na Tajikistan Emomali Rahmon a jiya Alhamis, inda suka amince da kulla dangantaka mai zurfi tsakanin kasashensu.
Emomali Rahmon na ziyara a kasar Sin tun daga ranar 30 ga watan Augusta zuwa 5 ga watan nan da muke ciki, bisa gayyatar Shugaba Xi Jinping.
Yayin ziyararsa a kasar Sin, zai halarci taron tattaunawa kan harkokin cinikayya da kasashe masu tasowa, da zai gudana a Xiamen dake kudu maso gabashin lardin Fujian na kasar Sin. (Fa'iza Mustapha)