Tuni sashen dake lura da ayyukan dakile annoba na ma'aikatar kula da lamurran al'umma, ya aike da jami'ai domin gudanar da ayyukan ceto, da na samar da sassauci ga wadanda ibtila'in ya shafa.
Zaftarewar kasar da ta auku da misalin 11 saura minti 20 na safiyar yau litinin, inda ta shafi iyalai 34. An kuma tabbatar da rasuwar mutane 2, yayin da kuma ake ci gaba da neman wasu mutanen 25 da suka bace. Kaza lika mahukunta sun samar da tallafin tantuna, da shimfidu domin amfanin wadanda aka tsugunar.