in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane biyu sun rasu a ibtila'in zabtarewar kasa na kudu maso yammacin kasar Sin
2017-08-28 19:19:28 cri
Mutane biyu sun gamu da ajalin su, kana wasu 25 sun bace sakamakon ibtila'in zabtarewar kasa da ya auku a kwaryar yankin Zhangjiawan dake garin Bijie, a lardin Guizhou dake kudu maso yammacin kasar Sin.

Rahotanni sun bayyana cewa, lamarin ya auku ne da sanyin safiyar yau Litinin da misalin karfe 11 saura minti 20, kuma ya shafi iyalai 34, tuni kuma aka fara ayyukan ceton rayuwan wadanda suka bace.

Ma'aikata dai sun riga sun gano gawawwakin mutane biyu, sun kuma cewo wasu mutanen 4 da lamarin ya rutsa da su, yayin da ake ci gaba da neman sauran mutane 25 da suka bace. A hannu guda mahukuntan dake lura da bala'u, sun riga sun samar da kayan tallafi da suka hada da tantuna, da shimfidu, domin amfanin wadanda aka tsugunar.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China