in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNHCR: yawan 'yan gudun hijira da ke shiga kasashen Turai ya ragu
2017-08-25 13:59:10 cri
Hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD wato UNHCR ta gabatar da wani rahoto a jiya Alhamis 24 ga wata, inda aka shaida cewa, yawan 'yan gudun hijira da bakin haure da suke shiga nahiyar Turai a watanni 6 na farko na shekarar 2017 ya ragu sosai, idan aka kwatanta da makamancin lokaci a shekara 2016, amma duk da haka matsalar azabtar da 'yan gudun hijirar ta yi tsanani, yayin da wasu ma suka riga suka mutu a hanyar su ta shiga nahiyar ta Turai.

An ce, bisa makamancin lokacin bara, yawan 'yan gudun hijira da bakin haure da suka tashi daga kasar Turkiya, da nufin ratsa bahar Rom zuwa kasar Girka ya ragu da kashi 94 cikin dari, amma yawansu dake tashi daga arewacin nahiyar Afirka zuwa kasar Italiya bai sauya ba.

Rahoton ya kara da cewa, a watanni 6 na farko na shekarar bana, yawan 'yan gudun hijira da bakin haure da suka mutu yayin da suke kokarin tashi zuwa nahiyar Turai ya yi kusan daidai da na bara, inda a kalla wasu 2253 ne suka rasa rayuka yayin da suke neman tsallake bahar Rom. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China