in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
IS ta yi wa mutane 11 yankan rago a harin da ta kai wani shingen bincike a Libya
2017-08-24 09:13:47 cri
Mayakan IS sun yi wa sojoji 9 da fararen hula 2 yankan rago yayin wani hari da suka kai kan wani shingen bincike a kudancin kasar Libya.

Kakakin rundunar sojin kasar Ahmad al-Mesmari, ya ce mayakan sun kai hari ne kofar Al-Fagha dake yankin Al-Jufra da safiyar jiya Laraba, inda suka yi wa sojoji 9 da fararen hula 2 yankan rago.

Shingen binciken na da nisan kilomita 500 daga kudancin birnin Tripoli.

Sojoji karkashin Janar Khalifa Haftar, sun shafe sama da shekaru 3 suna yaki da kungiyoyin 'yan ta'adda a gabashin Libya.

A farkon watan Yuli ne rundunar sojin ta sanar da kwace iko da garin Benghazi, birni mafi girma na biyu a Libya.

A kuma Cikin watan Decemban bara ne, dakarun da hadin gwiwar gwamnatin hadin kan kasar da MDD ke marawa baya, suka 'yanto Sirte, birnin dake da nisan kilomita 450 daga gabashin Tripoli, bayan shafe kusan watanni 7 suna gwabza fada da mayakan IS.

Sai dai, duk da wadannan nasarori da aka samu, har yanzu akwai ragowar mayakan IS a wasu sassan Libya. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China