Kwamishinan 'yan sandan jihar Enugu Danmallam Mohammed, ya ce ana samun yawaitar muggan makamai a hannun matasa har ma da manya a jihar.
Danmallam Mohammed wanda ya bayyana haka yayin taron yini daya kan tsaro da ya gudana tare da masu ruwa da tsaki, ya ce wannan mummunan al'amari ya haddasa tashe-tashen hankula da suka kai ga asarar rayukan 'yan Nijeriya maza da mata.
Ya shaidawa mahalarta taron cewa, 'yan sanda na gudanar da bincike kan zargin wasu munanan dabi'u da wasu kungiyoyi ke yi, da suka hada satar mutane don neman kudin fansa da fashi da makami da fyade da kisa da sauransu. (Fa'iza Mustapha)