in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sudan na fatan inganta huldar dake tsakaninta da kasar Sin
2017-08-22 10:03:28 cri
Ministan harkokin wajen Sudan Ibrahim Ghandour, ya ce Sudan na da nufin inganta huldar dake tsakaninta da kasar Sin yayin ziyarar mataimakin Firaministan Sin Zhang Gaoli dake karatowa.

Zhang Gaoli, zai isa birnin Khartoum a ranar Juma'a domin ziyarar yini biyu bisa gayyatar da mataimakin shugaban kasar na farko kuma Firaministan kasar Bakri Hassan Saleh ya yi masa.

Sanarwar da ministan harkokin wajen ya fitar, ta ce wannan muhimmin ziyara da babban jami'in kasar Sin zai kai, zai inganta huldar dake tsakanin Sudan da Sin tare da jadadda karfin dangantakarsu wanda ke samun tagomashi ta fuskar hadin gwiwar tattalin arziki dake tsakaninsu.

Zhang Gaoli ya isa Kuwait a jiya Litinin, domin fara ziyarar da yake zuwa kasashe 4, wanda zai kai shi Saudiyya da Sudan da kuma Namibia. (Fa'iza Msutapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China